An sace wasu mata biyu malaman coci a jihar Anambra

Rundunar yansandan jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya ta kaddamar da farautar wasu mata biyu malaman coci da aka sace a garin Ufuma da ke karamar hukumar Orumba ta Arewa a jihar.

Kwamishinan yansandan jihar, Nnaghe Oibono Itam, da mataimakinsa sun halarci wurin da lamarin ya faru tare da bayar da umarnin gaggauta nemo inda matan biyu suke, a cewar kakakin yansandan jihar.

Hakan na zuwa ne yan kwanakı bayan wani fitaccen malamin coci a jihar Father Emmanuel Opimma, da aka fi sani da Ebube Murinso, ya yi kira ga gwamnan jihar Anambra, Charres Soludo ya kawo ƙarshen matsalar tsaron da jihar ke tuskanta.

Yayin jawabinsa na sabuwar shekara, Father Obimma, ya bukaci Gwamna Soludo ya sauka daga muƙaminsa idan ba zai ya daƙile masu aikata laifukan da ke ci gaba da yaɗuwa a jihar ba.

– BBC Hausa

Comments (0)
Add Comment