An ɗaga wasan Najeriya da Libya

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka, CAF ta ɗage wasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da tawagar ƙasar Libya, wanda ya kamata a buga yau Talata.

Hukumar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar, inda ta ce ba za a fafata wasan ba, kamar yadda aka shirya fafatawa a daren yau.

An shirya fafata wasan ne na rukunin D a filin wasa na Martyrs of Benna da ke Benghazi, kafin tsaikon tarba tawagar Najeriya a ƙasar ya haifar da ce-ce-ku-ce, har ƴan wasan Najeriya suka koma gida.

Wannan matakin na CAF ya kwantar da fargabar da ake yi na ƙasar da za a ba nasarar a wasan, inda wasu magoya bayan wasan Super Eagles suka yi fargabar za a ba Libya nasara a wasan da ci uku da nema, kamar yadda ake yi idan abokin kara wa bai zo ba.

CAF ta ce ta tura lamarin zuwa kwamitin da abin ya shafa domin ɗaukar matakin da ya dace, tare da sanar da ranar da za a fafata wasan.

Comments (0)
Add Comment