Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya shigar da yara dubu 3, yawancinsu yayan talakawa, a manyan makarantu na musamman guda 2 dake kananan hukumomin Maiduguri da Jere.
Gwamnatinsa ce ta gina makarantun a yankunan kananan hukumomin Maiduguri da Jere dake da yaran dayawa da basa zuwa makaranta. An shirya makarantun da nufin kula da karatunsu.
- An soki yadda aka kafa Kwamatin Kidaya a Najeriya
- Ba da yawunmu wani tsagin tsohuwar CPC ya goyi bayan Tinubu ba – Malami
- Mutum 9 sun rasa rayukansu a Jihar Katsina
- Tinubu ya kara tsawaita ziyarar da yake yi a nahiyar Turai
- Kungiyar Afenifere ta soki matakin da gwamnatin Tinubu ta dauka kan wakar “Tell Your Papa”
Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Mallam Isa Gusau, ya fitar, tace gwamna Zulum ya sanar a ranar Litinin yayin bude makarantun cewa gwamnati zata mika su ga al’umma domin su gudanar da su, yayin da gwamnatin zata biya albashin malamai.
A wani cigaban kuma, gwamnan ya kaddamar da sabon titin da magudanan ruwa a unguwar Maromaro dake Maiduguri.