Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Alhamis, 1 ga watan Oktoba, a matsayin ranar hutu domin bikin cikar kasarnan shekaru 60 da samun yancin kai.
Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya ayyana hutun a madadin gwamnatin tarayya.
Babbar sakatariya a ma’aikatar cikin gida, Georgina Ehuriah, ta sanar da haka cikin wata sanarwar da ta fitar yau a Abuja.
- Matsalar wuta na ƙara ƙamari a jihohin Kano da makwabta
- Hatsarin mota ya yi sanadiyar mutuwar aƙalla mutum 5 a Jihar Gombe
- An ƙaddamar da shirin rigakafin cutar Polio a yankin tafkin Chadi
- Nan da wata 6 yankin Arewacin Najeriya zai fitar da matsayarsa kan zaben 2027 – Hakeem Baba Ahmad
- An soki yadda aka kafa Kwamatin Kidaya a Najeriya
Aregbesola ya taya daukacin yan Najeriya murnar cikar kasarnan shekaru 60 da yancin kai, inda ya tabbatar musu da jajircewar gwamnatin wajen habaka jin dadi da tattalin arzikin kasarnan.
Da yake taya yan Najeriya murna gudanar da bukukuwan yancin kan lafiya, ministan ya tunatar da cewa wadanda suka kwatowa kasarnan yanci, duk da banbancin addini, kabila da yare, sun hada kan su domin samun yancin kan kasa.