Helkwatar tsaro tace sojin sama na opearation Hadarin Daji sun lalata karin wani sansanin barayi tare da kashe batagari da dama a dajin Kwayanbana a jihar Zamfara.
Jagoran yada labaran ayyukan tsaro, John Enenche, cikin wata sanarwa da ya fitar yau a Abuja yace anyi luguden wuta ranar 7 ga watan Yunin da muke ciki, a cigaba da yakin sama da ake gudanarwa karkashin shirin operation accord.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Majon Janar Enenche yace an samu nasarar bayan wani rahoton sirri, leken asiri da sa’ido ya tabbatar da cewa an boye wasu tantuna a karkashin duhun bishiyoyin dajin.
Yace rahoton sirrin ya kuma bayyana cewa ana amfani da
kogo da ake samu a wajen a matsayin maboyar barayin tare da sanannen jagoransu,
Dogo Gede.